An Kawo Karshen Ebola A Laberia
Jun 09, 2016 06:48 UTC
Ma'aikatar lafiya a Laberia ta sanar da kawo karshen yaduwar annobar Ebola a kasar.
Laberia ta kasance kasa ta karshe inda cutar ta gagara tun dai bayan bullar ta a yammacin Afirka.
kasancewa kasar ta shafe kwanaki 42 ba tare da samun sabon kamuwa da cutar ba, hakan na nifin an sake dakile yaduwar cutar a cewar ministan lafiya na kasar.
Bisa ga sharidan hukumar lafiya ta duniya ana ayyana kawo karshen cutar Ebola a wata kasa idan har aka kwashe kwanaki 21 ba tare da samun sabon kamuwa da cutar ba.
Tags