Mayakan Boko Haram Sun Kashe mutane 4 A Jiya Asabar Da Yamma
Mayakan kungiyar yan ta'adda ta boko haram sun kashe mutane 4 a wani kauye kusa da birnin Maiduguri
Mayakan kungiyar yan ta'adda ta boko haram sun kashe mutane 4 a wani kauye kusa da birnin Maiduguri babban birnin Jihar Borno a Arewa maso gabacin tarayyar Nigeria.
Kamfanin dillancin labarai na Rasha Today ya ce a jiya da dare ne mayakan na Boko haran suka kai hari kan wani kayu kusa da birnin Maiduguri inda suka yanke mata gudu 4, wadanda suke tsakanin shekaru 28-48. Laifin wadan nan mata wa Boko haram shi ne mazajensu ko sunki aiki tare da Boko haram ko kuma suna zarginsu da tallafawa gwamnatin kasar a kansu.
Kungiyar Boko Haram dai ta fara fafatawa da jami'an tsaron Nigeria ne tun shekara 2009 kuma ya zuwa yanzu dubban mutane ne suka kashe a yankin Arewa maso gabancin Nigeria sun kuma tilastwa miliyoyi kauracewa gidajensu.