Benin Ta Rufe Ofisoshin Jakadanci 9
Kasar Benin TA Rufe Ofisoshin Jakadancinta 9 a Kasashe daban-daban na duniya
Kamfanin Dillancin Labarun Xinhua daga birnin Kotoko babban birnin kasar ta Benin, ya ambato ofishin shugaban kasar yana cewa;
Za a fure ofisoshin jakadanci biyar a cikin nahiyar Afirka, sai kuma guda a gabas ta tsakiya, sai wasu guda biyu a nahiyar Afirka.
Shugaban Ofishin Shugaban Kasar ta Benin Pascal Koupaki ya yi karin bayani da cewa ofisoshin jakadancin kasar da za a rufe a nahiyar Afirka sun hada Cote De Voire da Gabon da Congo, amma za a maida su zama kananan ofisoshin jakadanci.
Koupaki ya ci gaba da cewa; Daya daga cikin dalilan daukar wannan matakin shi ne rage kudaden da ta kasar ta kashe kashewa a harkar diplomasiyya.
Wasu matakan da kasar ta dauka sun kunshi rufe jami'an diplomasiyya masu wakiltar soja, da kuma rage yawan ma'aikatan.