'Yan Bindiga Sun Kashe Mutanen Kudu maso yammacin Najeriya 15
Jun 19, 2016 14:41 UTC
Najeriya: An Kashe mutane 15 A Jahar Ogun
Kamfanin Dillancin Labarun Xinhua na kasar Sin ya nakalto cewa; Wasu mutane dauke da makamai sun kai hari a yankin Ogijo da ke jahar Ogun, a kudu maso yammacin Najeriya inda su ka kashe mutane 15.
Tuni dai jami'an tsaro su ka fara gudanar da bincike domin gano maharan da kuma dalilinsa. Haka nan kuma majiyar 'yan sanda a yankin ta sanar da cewa abu ne mai yiyuwa a sami karuwar adadin wadanda su ka rasa rayukan nasu.
Kawo ya zuwa yanzu dai babu wanda ya dauki alhakin kai harin.
Tags