Tashin Nakiya ya hallaka Mutane 8 a Somaliya
Mutane 8 sun rasu sanadiyar tashin Nakiya a kusa da birnin Magadushu na kasar Somaliya
Tashar telbijin din Press Tv dake watsa shirye-shiryenta daga nan birnin Tehran ta nakalto Abdulkadir Muhamad wani Jami'in 'yan sanda na kasar Somaliyan ya ce Nakiyar ta tashi ne a yayin ficewar wata karamar Bas dake dauke da fasinja a garin Lefouli mai nisan kilomita 18 daga kudu maso gabashin magadushu fadar milkin kasar
Baya ga Mutanan da suka mutu a kwai wasu da dama da suka samu munanar raunuka.
Rahotanni sun ce an karfafa matakan tsaro a yankin kudancin kasar bayan kai wannan mumunan hari ga fararen hular.
A daren Juma'ar da ta gabata ma wata Nakiya ta tashi da wata karamar Bas dake dauke da fajinsa a kusa da hanya garin Lafourde dake kudu maso yammacin Magadushu,lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20.
A baya bayan nan dai kungiyar ta'addancin nan ta Ashabab ta tsananta kai hare-hare kan fararen hula a kasar Somaliyan