Najeriya : Masana Na Fargaban Fuskanci Yunwa A Arewa Maso Gabas
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i7876-najeriya_masana_na_fargaban_fuskanci_yunwa_a_arewa_maso_gabas
Tawagar masana dake sa ido akan rikicin da ake yi a shiyyar arewa maso gabashin Najeriya ta nuna damuwa akan alamun fuskantar fari a yankin saboda ayyukan ta'adin ‘yan kungiyar Boko Haram a yankin.
(last modified 2018-08-22T06:58:34+00:00 )
Jul 10, 2016 01:18 UTC
  • Najeriya : Masana Na Fargaban Fuskanci Yunwa A Arewa Maso Gabas

Tawagar masana dake sa ido akan rikicin da ake yi a shiyyar arewa maso gabashin Najeriya ta nuna damuwa akan alamun fuskantar fari a yankin saboda ayyukan ta'adin ‘yan kungiyar Boko Haram a yankin.

Masanan sun fadi a wata sanarwa cewa mutane sama da miliyan uku na cikin wani hali a yankin kuma suna bukatar taimako gaggawa.

Kungiyoyi irin wannan kan ayyana za’a sami fari muddin suka lura cewa kashi 20% na yankin da ake zance na fama da matsalar rashin abinci, da rashin lafiya da sauran matsalolin rayuwa.

Dubban rayukan jama'a ne dai suka salwanta a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya sakamakon hare-haren na 'yan kungiyar Boko Haram.