Taron Kungiyar Kasashen Larabawa Karo Na 27
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i8629-taron_kungiyar_kasashen_larabawa_karo_na_27
Yau Litinin ake bude taron koli na kungiyar kasashen larabawa karo na 27 a Nouakchott babban birnin kasar Mauritaniya.
(last modified 2018-08-22T11:28:39+00:00 )
Jul 25, 2016 06:46 UTC
  • Taron Kungiyar Kasashen Larabawa Karo Na 27

Yau Litinin ake bude taron koli na kungiyar kasashen larabawa karo na 27 a Nouakchott babban birnin kasar Mauritaniya.

Taron na kwanaki biyu  zai maida hankali kan batutuwan da suka shafi tsaro a kasashen musamen a Libya, Iraki, Yemen, Syria, da kuma Palestine.

Hakazalika taron zai duba yiwuwar kafa wata rundina hadin gwiwa kasashen don yaki da ta'adanci. 

kasashen dai na fatan fitar da wata sanarwa ta bai daya a taron domin samun karin hadin kai a tsakaninsu.

Wanda shi ne karon farko da Mauritaniya zata karbi bakuncin taron kungiyar tun bayan zamen ta mamba a shekara 1973, kuma ana sa ran shugaban kasar ne Mohamed Ould Abdel Aziz zai jagoranci kungiyar na tsawan shekaru biyu masu zuwa.