"Yanto Da Mutane Da Dama Daga Hannun 'Yan Bokoharam
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i865-yanto_da_mutane_da_dama_daga_hannun_'yan_bokoharam
Sojojin Najeriya Da Na Kamaru Sun 'Yanto da mutane masu yawa da kungiyar Bokoharam ta yi garkuwa da su.
(last modified 2018-08-22T06:57:49+00:00 )
Feb 16, 2016 09:26 UTC

Sojojin Najeriya Da Na Kamaru Sun 'Yanto da mutane masu yawa da kungiyar Bokoharam ta yi garkuwa da su.

Kakakin Sojan Najeriya Sani Usman ya fada a wani bayni da ya fitar cewa; A wani harin hadin guiwa a tsakanin sojojin Najeriya da Kamaru an kwato da mutane 112 da su ke karkashin kangin yan kungiyar ta Bokoharam.

Bayanin ya kunshi cewa; Mutanen da aka 'yanto a Jahar Borno da ke arewa maso gabacin kasar, sun kunshi maza 8 da mata 36 sai kuma kananan yara 68.

Kakakin Sojan na Najeriya ya ci gaba da cewa; "Yanto da mutanen ya zo ne a matsayin sakamakon hadin guiwa na kasashe biyu a fada da ayyukan ta'addanci.