"Yanto Da Mutane Da Dama Daga Hannun 'Yan Bokoharam
Feb 16, 2016 09:26 UTC
Sojojin Najeriya Da Na Kamaru Sun 'Yanto da mutane masu yawa da kungiyar Bokoharam ta yi garkuwa da su.
Kakakin Sojan Najeriya Sani Usman ya fada a wani bayni da ya fitar cewa; A wani harin hadin guiwa a tsakanin sojojin Najeriya da Kamaru an kwato da mutane 112 da su ke karkashin kangin yan kungiyar ta Bokoharam.
Bayanin ya kunshi cewa; Mutanen da aka 'yanto a Jahar Borno da ke arewa maso gabacin kasar, sun kunshi maza 8 da mata 36 sai kuma kananan yara 68.
Kakakin Sojan na Najeriya ya ci gaba da cewa; "Yanto da mutanen ya zo ne a matsayin sakamakon hadin guiwa na kasashe biyu a fada da ayyukan ta'addanci.
Tags