Sojojin Gwamnatin Somaliya Sun Kwato Wani Yanki Daga Mamayar 'Yan Al-Shabab
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i8926-sojojin_gwamnatin_somaliya_sun_kwato_wani_yanki_daga_mamayar_'yan_al_shabab
Sojojin gwamnatin Samaliya da hadin gwiwar dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afrika sun kwato yankin Gresan-Wain da ke kudu maso yammacin kasar daga mamayar 'yan kungiyar ta'addanci ta Al-shabab.
(last modified 2018-08-22T06:58:41+00:00 )
Jul 31, 2016 00:45 UTC
  • Sojojin Gwamnatin Somaliya Sun Kwato Wani Yanki Daga Mamayar 'Yan Al-Shabab

Sojojin gwamnatin Samaliya da hadin gwiwar dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afrika sun kwato yankin Gresan-Wain da ke kudu maso yammacin kasar daga mamayar 'yan kungiyar ta'addanci ta Al-shabab.

Jami'in gudanarwa a gwamnatin Somaliya Abdi Muhammad ya sanar da cewa: Sojojin gwamnatin Somaliya da hadin gwiwar dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afrika "AMISOM" a jiya Asabar sun samu nasarar kwato yankin Gresan-Wain da ke nisan kilomita 50 da yankin garin Hudhur a kudu maso yammacin kasar daga mamayar mayakan kungiyar ta'addanci ta Al-Shabab.

A gefe guda kuma wakili na musamman na kungiyar tarayyar Afrika a kasar Somaliya Francesco Madeira ya bayyana cewa: Tun daga lokacin tura dakarun wanzar da zaman lafiya da sulhu na kungiyar tarayyar Afrika a shekara ta 2007 zuwa yanzu an samu nasarar wanzar da zaman lafiya da sulhu a yankuna da dama na kasar Somaliya sakamakon ayyukan hadin gwiwar da ke gudana tsakanin sojojin gwamnatin Somaliya da dakarun kungiyar tarayyar Afrika ta "AMINSOM".