Ambaliyar Ruwan Sama Ta Ci Rayuka A Sudan
Ambaliyar Ruwan Sama Ta Ci Rayuka A cikin Gundumomi 13 A Kasar Sudan
Kamfanin Dillancin Labarun Xinhua na kasar Sin, daga kasar Sudan, ya nakalto ministan Harkokin cikin gida Ismat Abdurrahman, yana sanar da mutuwar 'yan kasar 76 sanadiyyar ambaliyar ruwan sama, tare kuma da rushewar gidaje 1300.
Ita ma hukumar bada agajin kasar ta Sudan, ta yi gargadi akan mummunan halin da mutane su ka shiga a yankunan da ambaliyar ta faru, tare da jaddada wajabcin ci gaba da ayyukan agaji.
Tuni dai majalisar dinkin duniya ta fitar da wani rahoto da a ciki ta bayyana cewa; yanayin el-nino da ke faruwa a cikin dabi'a na sauyin yanayi, zai sa a sami karin mutane miliyan 60 da za su fuskanci matsalar yunwa a duniya.