Sojojin Gwamnatin Somaliya Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Kungiyar Al-Shabab
Mahukuntan Somaliya sun tabbatar da labarin kashe daya daga cikin manyan kwamandojin kungiyar ta'addanci ta Al-Shabab a yankin Hiran da ke yammacin garin Beledweyne a kudu maso tsakiyar kasar.
Mataimakin gwamnan garin Hiran Muhammad Ibrahim Abdullahi a yau Asabar ya bayyana cewa: Dakarun sa-kai da suke tallafawa sojojin gwamnatin Somaliya sun yi bata kashi da mayakan kungiyar Al-Shabab a yankin Luuq Jeelow da ke nisan kilomita 20 da garin Beledweyne, inda suka yi nasarar kashe mayakan kungiyar Al-Shabab hudu ciki har da Abdi Adni daya daga cikin manyan kwamandojin kungiyar Al-Shabab.
Kwamandan rundunar sojin Somaliya ta musamman ta Somalia National Army {SNA} a takaice Janar Umar Adan Hassan ya sanar da cewa: Rundunar sojin Somaliya zata ci gaba da tallafawa dakarun sa- kai a kokarin da suke yi na kare kansu daga hare-haren wuce gona da irin kungiyar ta'addanci ta Al-Shabab. .