Kame Wani Kusa Na 'Yan tawayen Kasar Rwanda A D-Congo
An kame daya daga cikin jagororin 'yan tawayen kasar Rwanda a gabacin kasar D-Congo
Kamfanin Dillancin Labarun Xinhua na kasar Sin ya ce; An Kame Sabimana Iraguha wanda daya ne daga cikin jagororin kungiyar 'yan tawayen kasar Rwanda ta ( FDLR) a yankin Katiru da ke gundumar Kivo ta Arewa da ke gabacin kasar Jamhuriyar Demokradiyyar Congo.
Dama dai tuni ana neman Iraguha ruwa a jallo saboda laifukan kishan Kiyashi a kasar Rwanda, da kuma kashe sojojin kasar Jamhuriyar Demokradiyyar Congo.
Kwamandan bangaren sadarwa na sojojin D-Congo mai suna Guillaume Kaiko ya ce; Iraguha ya kashe sojojin kasar 32 a ranar 14 ga watan Mayu na 2013 a kauyen Bunyakiri da ke gundumar Kivo ta Kudu.
Sojojin kasar ta D-Congo sun yi kira ga dukkanin 'yan tawayen da ke gabacin kasar da su mika kai.
Gabacin kasar D-congo dai tunga ce ta 'yan tawayen cikin gida da kuma na kasashen makwabta.