RDC : Jami'an Tsaro Sun Murkushe Masu Zanga-zanga
Aug 17, 2016 06:34 UTC
'Yan sanda da sojoji a Jamhuriya demukuradiyyar Kongo, sunyi amfani da hayaki mai sa kwalla da kuma harbin tsoratarwa domin tarwatsa masu masu zanga zanga a Beni.
Mutanen yankin dai na zanga-zanga ne domin kalubalantar gwamnatin kasar akan rashin tabaka komai akan rikice rikice dake shafar yankin.
Wannan dai na zuwa ne a kwana na karshe na zamen makoki da ake a kasar bayan kisan da wasu mayaka da ake zargi da cewa 'yan Uganda ne suka kai a wannan yankin na Beni dake gabashin kasar inda suka kashe mutane 51.
Tags