Jawabin Jagoran Juyin Musulunci Akan Makon Tsaro
https://parstoday.ir/ha/news/iran-i11410-jawabin_jagoran_juyin_musulunci_akan_makon_tsaro
Jagora: Dacen Da Iran ta samu a wannan lokacin tushensa sadaukar da kai na shahidai.
(last modified 2018-08-22T06:58:58+00:00 )
Sep 22, 2016 15:34 UTC
  • Jawabin Jagoran Juyin Musulunci Akan Makon  Tsaro

Jagora: Dacen Da Iran ta samu a wannan lokacin tushensa sadaukar da kai na shahidai.

A cikin sakon da ya fitar a yau alhamis dangane da makon tsaro, jagoran juyin musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamnei   ya bayyana cewa; Dacen da al'ummar Iran su ka samu a wannan lokacin tushensa jagorancin shahidai da wadanda su ka sadaukar da kawukansu.

 Sakon na Jagoran juyin musulunci na Iran ya ci gaba da cewa; Rayuwa da mutuwar shahidai ita ce ta bai wa al'ummar musulmi daukaka.

 Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya kuma bayyana cewa; Muna godiya ga Allah da cewa a zamaninmu ne ma'anar koli ta shahada ta bayyana kuma zukata masu tsarki su ka zama suna shaukinta.

A jiya laraba ne dai 31 ga watan Shahribar na hijira shamshiyya aka fara makon tsaro, da ya zo daidai da lokacin harin da Saddam na Iraqi ya kawo wa Iran.