Jagora: Dolene Sojojin Kasar Iran Su Sami Kwarewar Kare Kasar
https://parstoday.ir/ha/news/iran-i11698-jagora_dolene_sojojin_kasar_iran_su_sami_kwarewar_kare_kasar
Jagoran juyinn juya halin musulunci a nan Iran Ayatullah Sayyid Aliy Khamenei ya bayyana cewa dole ne sojojin kasar Iran su kasance suna da korewa da kuma karfin kare kasar daga baranar makiya a ko da yauce.
(last modified 2019-01-16T07:30:45+00:00 )
Sep 28, 2016 17:50 UTC
  • Jagora: Dolene Sojojin Kasar Iran Su Sami Kwarewar Kare Kasar

Jagoran juyinn juya halin musulunci a nan Iran Ayatullah Sayyid Aliy Khamenei ya bayyana cewa dole ne sojojin kasar Iran su kasance suna da korewa da kuma karfin kare kasar daga baranar makiya a ko da yauce.

 Jagoran ya bayyana haka ne a yau Laraba a lokacinda yake halattar bukin yaye sojojin a makarantar sojoji ta Imam Husain (a) dake nan Tehran. Tashar television ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jagoran yana cewa " a halin yanzu kasar Iran tana fuskantar baraza daga bangarori da dama don irin matsayin da ta dauka na kare addinin musulunci da kuma kasancewa 'yentacciyar kasa a duniya. Don haka sojojin kasar dole ne su kasance cikin shirin aiwatar da abinda ya hau kansu a dok lokacinda bukatar haka ta taso.

Ayatollah Khamenei ya ce yakin shekaru 8 wanda sojojin kasar suka tabka da sojojin kasar Iraqi ya zama wani dame na nuna kwarewa da kuma gogewa a harkokin yaki ga sojojin kasar don haka bai kamata su manta da wannan korrewar ba musaman a lokacinda kasar take fuskantar barazana daga bangarori daban daban a duniya.