Rauhani: Azumi Jarabawa Ce Ta Allah Domin Tarbiyantar Da Ruhin Musulmi
Shugaba Hassan Rauhani na Iran bayyana ibadar azumi a matsayin daya daga cikin manyan ayyukan ibada da ke a matsayin jarawa ta ubangiji ga musulmi, domin tsarkake ruhinsu a kan hakuri, tausaya wa marassa karfi, kaskantar da kai wajen bin umarnin Allah, tare da hana rai abin da yake bukata.
Shugaba Rauhani ya bayyana hakan ne a daren jiya a lokacin da ya halarci wani cin abincin buda baki da aka gayyace shi a cikin Tehran.
A lokacin da yake gabatar da jawabi a wurin, shugaba Rauhani ya bayyana cewa, Allah ya wajabta azumi a kan musulmi ne domin su samu kamala ta tsoron Allah, wadda ita ce mabudin samun dukkanin rabo na duniya da lahira.
A jiya ne kwamitin kare kundin tsarin mulki a Iran ya tabbatar da zaben da aka yi wa shugaba Rauhani, inda ya lashe fiye kashi 58 cikin dari na dukkanin kuri'un da aka kada a lokacin zaben.