Majalisar Dokokin Kasar Iran Ta Tube Ministan Kwadago Daga Mukaminsa
https://parstoday.ir/ha/news/iran-i32677-majalisar_dokokin_kasar_iran_ta_tube_ministan_kwadago_daga_mukaminsa
Majalisar dokokin kasar Iran ta tube ministan gwadago da kamfanono Ali Rabiei daga mukaminsa bayan ya kasa gamsar da su dangane da yadda lamuran tattalin narzikin kasar suka lalace a cikin yan kwanakin da suka gabata.
(last modified 2018-08-22T11:32:13+00:00 )
Aug 08, 2018 11:56 UTC
  • Majalisar Dokokin Kasar Iran Ta Tube Ministan Kwadago Daga Mukaminsa

Majalisar dokokin kasar Iran ta tube ministan gwadago da kamfanono Ali Rabiei daga mukaminsa bayan ya kasa gamsar da su dangane da yadda lamuran tattalin narzikin kasar suka lalace a cikin yan kwanakin da suka gabata.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a safiyar yau Laraba ne ministan ya je gaban majalisar don kare kansa a kan korafe korafen majalisan kan yadda yake tafiyar da ma'aikatarsa. musamman ganin yadda kudaden kasar Rial suka fadu da kashi kimani 80% idan kan kwatantan da dalar Amurka. 

Labarin ya kara da cewa yan majalisa 129 suka bukaci a tsige ministan a yayinsa da 111 suka goyi bayansa sannan wasu 3 suka ki kada kiri'insu.