Bunkasar Alakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Iran Da Malaysia
Jakadiyar kasar Iran a kasar Malaysia ta bayyana gagarumin ci gaban da aka samu a tsakanin Iran da Malaysia ta fuskar harkokin tattalin arziki da cinikayya.
Kmafanin dillancin labaran Irna ya bayar da rahoton cewa, a yau jakadiyyar kasar Iran a Malaysia Mardiya Afkham ta gana da shugaban majalisar dattijan kasar ta Malaysia a birnin Kualalampour fadar mulkin kasar, inda suka tattauna muhimamn batutuwa da suka shafi alaka a tsakanin kasashen biyu.
Shugaban majalisar dattijan kasar Malaysia S. Vigneswaran ya bayyana alaka a tsakanin kasarsa da Iran da cewa, alaka ce ta tarihi, kuma tana samun ci gaba a wanann lokaci fiye da kowane lokaci, musamamn ta fuskar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin kasashen biyu.