Zarif Zai Ziyarci Wasu Kasashen Latine Amurka
Aug 18, 2016 11:11 UTC
Ministan harkokin wajen kasar Iran, Muhammad Javad Zarif zai fara wani ran gadi a wasu kasashen Latine Amurka guda shida a wannan Lahadin.
Wannan ziyara ta Mr Zarif nada nufin karfafa alaka da kasashen ta fuskar siyasa da kuma tattalin arziki.
Mr Zarif ya bayyana hakan ne ta shafinsa na Twitter a harshen turancin Ingila da kuma Spaniya.
koda yake bayanin bai zayyano kasahen da Mr Zarif zai ziyarta ba kawo yanzu, amma dai zai kasance tare da rakiyar wata babbar tawaga ta 'yan kasuwa da masu zuba jari na kasar ta Iran.
Tags