Kasar Masar Ta Kafa Sharuddan Maida Alaka Da Turkiya
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i10093-kasar_masar_ta_kafa_sharuddan_maida_alaka_da_turkiya
Kakakin Ma'aikatar Harkokin Wajen Masar ya ce; Da akwai sharudda domin mayar da alaka da Turkiya
(last modified 2018-08-22T06:58:49+00:00 )
Aug 24, 2016 07:51 UTC
  • Kasar Masar Ta Kafa Sharuddan Maida Alaka Da Turkiya

Kakakin Ma'aikatar Harkokin Wajen Masar ya ce; Da akwai sharudda domin mayar da alaka da Turkiya

Kakakin Ma'aikatar Harkokin Wajen Masar ya ce; Da akwai sharudda domin mayar da alaka da Turkiya

Mai magana da yawun  ma'aikatar harkokin Wajen kasar ta Masar Ahmad Abu Zaid, ya ce; Masar tana maraba da duk wani yunkuri na gaskiya da Turkiya za ta nuna domin mayar da alaka a tsakaninsu.

Ahmad Abu Zaid ya kara da cewa; Kyautata alaka a tsakanin kasashen Masar da Turkiya za ta amfani dukkanin kasashen biyu.

Alaka dai a tsakanin Masar da Turkiya ta yi kamari tun bayan kifar da gwamnatin Muhammadu Mursi da Tukiyan ta ke goyawa baya.