Masar: Karuwar Adadin Wadanda Su ka Rasa Rayukansu A Harin Alqahira.
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i15136-masar_karuwar_adadin_wadanda_su_ka_rasa_rayukansu_a_harin_alqahira.
Harin Ta'addanci A Kasar Masar
(last modified 2018-08-22T06:59:23+00:00 )
Dec 11, 2016 15:38 UTC
  • Masar: Karuwar Adadin Wadanda Su ka Rasa Rayukansu A Harin Alqahira.

Harin Ta'addanci A Kasar Masar

Ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar Masar, ta sanar da cewa; Adadin wadanda su ka rasa rayukansu sanadin harin ta'addancin da aka kai a wata majami'a a birnin alqahira sun karu zuwa 20.

 Ma'aikatar kiwon lafiyar ta Masar ta ci gaba da cewa; A halin da ake ciki a yanzu ana bada taimakon da ya dace ga wadanda su ka jakkata a sanadin harin.

Da safiyar yau ne dai aka sanar da tashin wasu abubuwa a cikin majami'ar Saint Marck da ke unguwar Abbasiyya a cikin birnin alqahira. Sanarwar farko ta ce mutane biyar ne su ka kwanta dama.

Masar ta fada cikin matsalolin tsaro tun faduwar gwamnatin Muhammadu Mursi a 2013.