Iraki : Hare-hare IS Sun Yi Ajalin Mutum A Kalla 52
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i24039-iraki_hare_hare_is_sun_yi_ajalin_mutum_a_kalla_52
Kungiyar 'yan ta'adda ta IS ko kuma Da'esh ta dauki alhakin kai jerin hare-haren da suka yi sanadin mutuwar mutane a kalla 52 a kusancin Bagadaza babban birnin kasar.
(last modified 2018-08-22T11:30:41+00:00 )
Sep 14, 2017 16:03 UTC
  • Iraki : Hare-hare IS Sun Yi Ajalin Mutum A Kalla 52

Kungiyar 'yan ta'adda ta IS ko kuma Da'esh ta dauki alhakin kai jerin hare-haren da suka yi sanadin mutuwar mutane a kalla 52 a kusancin Bagadaza babban birnin kasar.

Ko baya ga wadanda suka rasa rayukansu da akwai wasu sama da 90 da suka raunana, a yayin da wasu bayanai ke cewa akwai yiyuwar adadin wadanda suka mutu ya karu saboda munanen raunukan da suka samu.

Hare-haren wadanda aka kai da bindiga da kuma mota an dai kai su ne a wani gidan cin abunci dake birnin Nassiriya a nisan kilomita 300 daga birnin Bagadaza a yankin Zi Qar wanda yanki ne da ba'a cika samun tashe tashe hankula ba.

Harin na biyu kuwa wanda aka kai da mota an kai shi ne a wani shingen bincike na jami'an tsaro dake kan wata babbar hanya inda masu yawan bude ido da masu ziyara ke bi zuwa wurare masu tsarki na 'yan shi'a a biranen Najaf da Karbala.

A cikin wata gajeriya sanarwa data wallafa a shafinta na farfaganda Amaq, kungiyar 'yan ta'adda ta Da'esh ta ce i'yan kunar bakin wakenta da dama ne suka kai harin.