Dala Biliyan 8 Ta Fice Daga Nahiyar Afirka A Shekara Guda
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i4399-dala_biliyan_8_ta_fice_daga_nahiyar_afirka_a_shekara_guda
Dala Biliyan 8 ce Ta Fice Daga Nahiyar Afirka A Shekara Guda.
(last modified 2018-08-22T06:58:11+00:00 )
Apr 26, 2016 07:33 UTC
  • Dala Biliyan 8 Ta Fice Daga Nahiyar Afirka A Shekara Guda

Dala Biliyan 8 ce Ta Fice Daga Nahiyar Afirka A Shekara Guda.

An bayyana cewa a kowace shekara nahiyar Afirka tana asarar Dala Biliyan 8 na hannun jarinta.

Kamfanin Dillancin Labarun Xinhua ya ambato tsohon shugaban kasar Afrika ta Kudu, Thabo Mbeki yana cewa; Abin takaici ne cewa a kowace shekara dalar Amurka biliyan 8 ce ta ke ficewa daga nahiyar Afirkan ta hanyar da ta sabawa doka.

Tsohon shugaban kasar Afirka ta kudun ya ci gaba da cea; Wajibi ne a samo hanyoyin da za a dauka domin hana ficewar makudan kudaden na hannun jari daga cikin nahiyar ta Afirka.

Babban Bankin Bada Lamuni Na Duniya ma dai ya fitar da wani rahoto da a ciki ta bayyana asarar makudan kudaden da nahiyar ta Afirka ta ke yi a kowace shekara.