Harin Ta'addancin Kungiyar Da'ish A Birnin Riyad Na Kasar Saudiyya
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i508-harin_ta'addancin_kungiyar_da'ish_a_birnin_riyad_na_kasar_saudiyya
Kungiyar ta’addanci ta Da’ish ta dauki alhakin kai harin bom a birnin Riyad fadar mulkin kasar Saudiyya a jiya Litinin.
(last modified 2018-08-22T06:57:47+00:00 )
Feb 09, 2016 02:58 UTC
  • Harin Ta'addancin Kungiyar Da'ish A Birnin Riyad Na Kasar Saudiyya

Kungiyar ta’addanci ta Da’ish ta dauki alhakin kai harin bom a birnin Riyad fadar mulkin kasar Saudiyya a jiya Litinin.

Majiyar rundunar ‘yan sandan Saudiyya a jiya Litinin ta sanar da cewa; Motar wani mutum ta tarwatsewa a kofar gidansa da ke yankin Aziziyya amma dai babu hasarar rai da tarwatsewar motar ta janyo, sai dai konewar wasu motoci da suke wajen da bom din ya tashi.

A bayan faruwar tarwatsewar bom din kungiyar ta’addanci ta Da’ish ta fitar da bayanin cewa; Ita ce ke da alhakin dana bom din a jikin motar a kokarin da kungiyar key i na halaka mai motar saboda kasancewarsa jami’in tsaron kasar ta Saudiyya.

A ranar 29 ga watan Janairun da ya gabata ma kungiyar ta’addanci ta Da’ish ta kai wani mummunan harin wuce gona da iri kan Masallacin ‘yan shi’a a yankin Sharkiyya na kasar ta Saudiyya, inda harin yay i sanadiyyar mutuwar mutane 4 tare da jikkata wasu 18 na daban.