Halakar 'Yan'taadda Fiye da 40 A Kasar Masar.
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i595-halakar_'yan'taadda_fiye_da_40_a_kasar_masar.
Fiye Da 'yan ta'adda 40 ne su ka halaka a yankin Sina na kasar Masar.
(last modified 2018-08-22T11:27:47+00:00 )
Feb 11, 2016 05:33 UTC
  • Halakar 'Yan'taadda Fiye da 40 A Kasar Masar.

Fiye Da 'yan ta'adda 40 ne su ka halaka a yankin Sina na kasar Masar.

Kamfanin Dillancin Labarun Spotik na kasar Rasha ya ambato cewa; A jiya laraba jiragen sama masu saukar angulu sun yi aman wuta a wata mabuya ta 'yan ta'addar kungiyar Da'esh a yankin Sina.

Sojan Masar Sun sanar da cewa; Sun kai harin ne bayan wani hari da aka kai wa motarsu ta soja a kudancin garin Sheik Zuwaid. Harin na sojan Masar ya yi wa 'yan ta'addar asara mai yawa.

Tun a cikin watan Decemba na 2013 ne sojojin Masar su ka bude kai hare-hare masu tsanani akan kungiyoyin da su ke dauke da makamai a yankin Sina ta arewa.