Majalisar Dokokin Turkiyya Ta Amunce Da Dawo Da Alaka Da Israila
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i9898-majalisar_dokokin_turkiyya_ta_amunce_da_dawo_da_alaka_da_israila
Majalisar dokoki a Turkiyya ta amunce da dawo da huldar diflomatsiya da Israila, bayan shafe shekaru shida na rashin jituwa.
(last modified 2019-04-27T14:25:10+00:00 )
Aug 20, 2016 10:58 UTC
  • Majalisar Dokokin Turkiyya Ta Amunce Da Dawo Da Alaka Da Israila

Majalisar dokoki a Turkiyya ta amunce da dawo da huldar diflomatsiya da Israila, bayan shafe shekaru shida na rashin jituwa.

A karshen watan Yuni daya gabata ne kasashen biyu suka cimma matsaya ta dawo da hulda tsakaninsu, kafin daga bisani a mika kudirin ga majalisar dokokin kasar wace ta amunce dashi a cikin daren jiya Juma'a.

A bisa yarjejeniyar da kasashen biyu suka cimma, Israi'la zata biya Turkiyya diyya ta kudade da yawan su ya kai $ Amurka Miliyan 20 bayan wani farmaki da Israila ta kaiwa wani jirgin ruwan kasar a gabar zirin Gaza a cikin shekara 2010, inda Turkiyawa 10 suka mutu.

Sannan a nata bangare ita kuwa Turkiyya zata janye tuhumar da take yiwa wasu tsaffin kwamandodin sojin Israi'a dake da hannu a farmakin na wacen lokacin.