WHO: Za'a Fara Gwajin Rigakafin Cutar Malaria A Wasu Kasashen Afirka
Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta sanar da cewa za ta fara gwajin rigakafin cutar zazzabin cizon sauro (malaria) a kasashe uku na Afirka da suka hada da kasashen Ghana, Kenya da kuma Malawi.
Sanarwar da hukumar ta WHO ta fitar ta kara da cewa a shekara mai zuwa ne za a fara gwajin rigakafin a wadannan kasashe ukun ne don gwaja allurar rigakafin saboda shirye-shiryen da suke da shi na magance cutar saboda suna daga cikin kasashen da suke fama da cutar malaria din.
Sanarwar ta kara da cewa a lokacin da za a kammala wannan shirin dai a shekara ta 2020 za a samun nasarar yi wa kananan yara da jarirai 360,000 allurar, wato a takaice a kowace kasa za a iya yi wa yara kimanin 120,000 allurar kenan musamman a yankunan da cutar ta fi yawa.
Kididdiga dai ta nuna cewa a kowace shekara kimanin mutane 500,000 ne suke rasa rayukansu a duk fadin duniya saboda kamuwa da cutar ta malariya, mafiya yawansu kuwa sun fito ne daga kasashen Afirka inda kananan yara suka fi mutuwa.