Spain: 'Yan gudun Hijira Daga Afirka 600 Sun Tsira Daga Mutuwa
https://parstoday.ir/ha/news/world-i25540-spain_'yan_gudun_hijira_daga_afirka_600_sun_tsira_daga_mutuwa
Ma'aikatan agaji na kasar Spain ne suka sanar da ceto da 'yan gudun hijirar da suka fito daga nahiyar Afirka a gabar ruwan kasar.
(last modified 2018-08-22T11:31:00+00:00 )
Nov 19, 2017 06:47 UTC
  • Spain: 'Yan gudun Hijira Daga Afirka 600 Sun Tsira Daga Mutuwa

Ma'aikatan agaji na kasar Spain ne suka sanar da ceto da 'yan gudun hijirar da suka fito daga nahiyar Afirka a gabar ruwan kasar.

Sanarwar ta ci gaba da cewa a halin da ake ciki ana ci gaba da aikin ceton mutanen daga halaka.

Tun a jiya asabar ne dai sanarwar ta ce 'yan gunun hijirar sun fito ne daga kasar Libya domin shiga cikin kasashen turai inda suka fuskanci halaka a yankin Mursiya da ke kudu masu gabacin kasar Spain.

A bisa kididdigar hukumar 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ( IOM) kusan mutane 160,000 ne suka bi ta hanyoyi masu hatsari domin yin hijira zuwa Afirka a wannan shekara, kuma kusan 3000 daga cikinsu sun mutu.