Catalonia: Masu Neman Ballewa Sun Lashe Zaben Majalisar Dokoki
https://parstoday.ir/ha/news/world-i26591-catalonia_masu_neman_ballewa_sun_lashe_zaben_majalisar_dokoki
Jam'iyyun da suke goyon bayan 'yancin yankin Catalonia na kasar Spain sun sami nasara a zaben 'yan Majalisar dokokin da aka yi a yanki da kujeru 70 a jumillar 135.
(last modified 2019-08-10T14:54:46+00:00 )
Dec 22, 2017 06:39 UTC
  • Catalonia: Masu Neman Ballewa Sun Lashe Zaben Majalisar Dokoki

Jam'iyyun da suke goyon bayan 'yancin yankin Catalonia na kasar Spain sun sami nasara a zaben 'yan Majalisar dokokin da aka yi a yanki da kujeru 70 a jumillar 135.

An rusa tsohuwar majalisar wacce ita ma masu son ballewar suke da rinjaye a cikinta.

Tsohon shugaban majalisar dokokin, Carles Puigdemont wanda jam'iyyarsa tana cikin wadanda suka sami nasara, ya bukaci ganin an wanke shi daga tuhumar da aka yi masa a baya.

A halin da ake ciki Puigdemont yana zaman hijira a kasar Belgium, ya kuma bukaci ganin an saki wasu jami'an gwamnatin yankin na catalonia da ake tsare da su a cikin kasar ta Spain.

Yankin na Catalonia wanda yake arewa maso gabacin kasar Spain ya dade yana fafutukar samun 'yanci daga kasar.