Turai Na Farautar Masu Safarar Bakin Haure Dubu 35
https://parstoday.ir/ha/news/world-i29660-turai_na_farautar_masu_safarar_bakin_haure_dubu_35
Mahukumtan kungiyar tarayyar Turai na neman kimanin masu safarar bakin haure zuwa nahiyar su dubu 65, adadin da ya rubanya sau biyu a cikin shekaru 3 da matsalar kwararar bakin hauren ta ta’azara a nahiyar.
(last modified 2018-08-22T07:01:39+00:00 )
Apr 06, 2018 01:56 UTC
  • Turai Na Farautar Masu Safarar Bakin Haure Dubu 35

Mahukumtan kungiyar tarayyar Turai na neman kimanin masu safarar bakin haure zuwa nahiyar su dubu 65, adadin da ya rubanya sau biyu a cikin shekaru 3 da matsalar kwararar bakin hauren ta ta’azara a nahiyar.

Cikin wata sanarwar da hukumar yaki da masu fasa kwabrin bakin haure ta turai ta  fitar ta ce duk da nasarar da aka samu na raguwar yawan bakin hauren dake yi nasarar kutsa kai a nahiyar turai ta hanyar  tekun Medetaraniyan a 2016, har yanzu matsalar  na nan daram, 

A binciken da mahukumtan kasashen turan suka bada umarnin gabatarwa, ya nuna cewa, yanzu haka sannu a hanakli ana ci gaba da tantance masu aikata wannan laifi

Robert Crepinko, shugaban sashen dake kula da shige da ficen baki na nahiyar turai ya sanar da AFP cewa, a karshen shekarar da ta gabata suna da sunayen kimanin masu safarar bakin hauren zuwa turai dubu 65 akan girgam

A shekara ta 2015 yawan masu wannan aiki na laifi su dubu 30 ne, kafin su zama dubu 55 a 2016, a yayin da a shekarar 2017 da ta gabata yawansu ya karu da dubu 10 inda ajimilce suka  kai dubu 65.