Birtaniya Ta Kafa Kwamitin Ficewa Daga Turai.
https://parstoday.ir/ha/news/world-i7330-birtaniya_ta_kafa_kwamitin_ficewa_daga_turai.
Pira ministan Birtaniya Ya sanar da kafa Kwamitin Bin diddigin Ficewa daga tarayyar turai.
(last modified 2018-08-22T06:58:30+00:00 )
Jun 27, 2016 14:30 UTC
  • Birtaniya Ta Kafa Kwamitin Ficewa Daga Turai.

Pira ministan Birtaniya Ya sanar da kafa Kwamitin Bin diddigin Ficewa daga tarayyar turai.

David Cameroon ya fada a yau litinin cewa majalisar zartarwa ta amince da kafa wani kwamiti wanda zai bi diddigin ficewar kasar daga cikin tarayyar turai.

Cameroon ya ci gaba da cewa; Bisa la'akari da cewa sakamakon zaben raba gardama a kasar, na ficewa daga tarayyar turai, an kafa kwamiti da wakilci daga ma'aikatun kasuwanci da baitul-mali da ma'aikatar harkokin waje domin bin diddigin ficewa daga tarayyar ta turai.

Bugu da kari, Dadiv Cameroon ya ce zai halarci taron kungiyar tarayyar turai din wanda za a yi a gobe, inda a can ma zai tattauna batun ficewar kasar tasa.