-
Majalisar Dinkin Duniya Ta Zame 'Yar Kallo Dangane Da Zaluncin Haramtacciyar Kasar Isra'ila
Feb 27, 2017 00:37A rahoton da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar yana dauke da cewa: Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra'ila ta rusa gidajen Palasdinawa masu yawa a yankunan Palasdinawa da suke gabar yammacin kogin Jordan a makon da ya gabata lamarin da ya kara janyo rashin matsuguni ga Palasdinawa masu tarin yawa.
-
Magajin Garin Birnin Boston Na Amurka Ya Nuna Goyon Baya Ga Musulmi
Feb 26, 2017 08:46Magajin garin birnin Boston na kasar Amurka ya nuna rashin amincewarsa da duk wani mataki na takura ma musulmi, tare da shan alwashin taimaka ma musulmi 'yan gudun hijira da suke zaune a birnin.
-
Jami'an Diflomasiyyar Turkiya 136 Sun Nemi Mafakar Siyasa A Jamus
Feb 26, 2017 03:14Jami'an diflomasiyyar kasar Trkiya 136 ne suka nemi mafakar siyasa daga gwamnatin kasar Jamus, wadanda dukkaninsu suna dauke ne da fasfo na diflomasiyya.
-
Wata Musulma Ta Ajiye Aikinta A White House Saboda Siyasar Trump
Feb 25, 2017 09:46Wata mata musulma da take aiki a fadar white house a Amurka, ta ajiye aikinta domin nuna rashin amincewa da salon bakar siyasa ta kin jinin musulmi irin ta Donald Trump.
-
Rasha Ta Ce Za Ta Yi Watsi Da Duk Wani Sabon Takunkumi A Kan Syria
Feb 25, 2017 09:45Gwamnatin kasar Rasha ta yi barazanar hawa kujerar naki dangane da duk wani yunkurin kakaba wasu sabbin takunkumai a kan kasar Syria a kwamitin tsaron majalisar dinkin duniya.
-
Asusun IMF Ya Amince Da Wasu Shawarwari Na Bankin Muslunci
Feb 25, 2017 09:44Asusun bayar da lamuni na duniya IMF ya amince da wasu daga cikin shawarwarin da bankin musulunci ya gabatar dangane da harkokin kudade a bankuna.
-
Rasha Ta Ce Zata Hana Fitar Da Kuduri Kan Gwamnatin Siriya Dangane Da Zargin Amfani Da Muggan Makamai
Feb 25, 2017 03:04Gwamnatin Rasha ta sanar da cewa: Zata hau kan kujerar naki domin hana fitar da duk wani kuduri kan zargin gwamnatin Siriya da yin amfani da muggan makamai a yakin da take yi da 'yan ta'addan kasa da kasa da aka jibge a cikin kasarta.
-
Hukumar Makamashin Nukiliya Ta Kasa Da Kasa Ta Tabbatar Da Cewa Iran Tana Aiki Da Yarjejeniya.
Feb 24, 2017 15:38A yau juma'a ne hukumar makamashin Nukiliya ta kasa da kasar ta fitar da rahota a ciki ta tabbatar da cewa; Iran tana rage yawan tataccen sanadin urani'um fiye da yadda yarjejeniyar Nukiliya ta kunsa.
-
Kungiyar Amnesty Int. Ta Yi Kakkausar Suka Kan Cin Zarafin 'Yan Adam Myanmar
Feb 24, 2017 09:05Kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty Int. ta yi Allawadai da kakakusar murya dangane da kisan kiyashin da aka yi wa musulmi a Myanmar.
-
Isra'ila, Al-Sa'ud Da Al-Khalifa: Tushen Laiffuffukan Yaki Da Take Hakkokin Bil'adama
Feb 24, 2017 01:20Laifin yaki na daga cikin muhimman laifuffukan da aka yi bayanin ma'anarsa a fili ciki takardu da dokokin kotunan kasa da kasa. Sashi na 8 na dokokin hukunta laifuffukan na kasa da kasa yayi bayanin abubuwan da suke tabbatar da laifin yaki, wanda daga cikinsu akwai kisan gilla, azabtarwa mai tsanani, cutar da jikin mutum, kai hari da gangan kan fararen hula, ruwan bama-bamai kan gidajen mutane ko gine-ginen da ba na soji ba da kuma amfani da makamai masu guba da iskar gas mai makure mutum.