Zanga-zangar neman sakin Sheikh El-zakzaky A Afirka Ta kudu
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i1-zanga_zangar_neman_sakin_sheikh_el_zakzaky_a_afirka_ta_kudu
Mutanen Kasar Afirka Ta Kudu Sun gudanar da Zanga-zangar neman sakin shugaban harkar musulunci na Najeriya Sheikh Yakubu Ibrahim el-zakzaky.
(last modified 2018-08-22T11:27:44+00:00 )
Jan 30, 2016 17:24 UTC
  • Zanga-zangar neman sakin Sheikh El-zakzaky A Afirka Ta kudu

Mutanen Kasar Afirka Ta Kudu Sun gudanar da Zanga-zangar neman sakin shugaban harkar musulunci na Najeriya Sheikh Yakubu Ibrahim el-zakzaky.

Tashar telbijin din Press tv, ta watsa rahoto akan zanga-zangar da mutanen Afika ta kudu suka yi, suna masu neman a sakin sheikh Yakubu Ibrahim El-zakzaky da ake tsare da shi a Najeriya.

Masu Zanga-zangar dai sun taru a bakin ofishin Jakadancin Najeriya da ya ke a birnin Pretoria dauke da kwalayen da aka rubuta yin kira da a saki malamin na addinin musulunci.

Kusan watanni biyu kenan da sojojin Najeriya su ka kai hari a cibiyar kungiyar 'yan'uwa musulmi da ke birnin Zari'a a jahar kaduna, tare da rushe gidan sheik Ibrahim Yakubu el-zakzaky.

Kawo ya zuwa yanzu kungiyar ta fitar da sunayen mutane fiye da 700 tsakanin wadanda aka kashe da kuma wadanda ake tsare da su.