Sabuwar Gwamnatin Tunisiya Ta Saba Layar Kama Aiki
Aug 27, 2016 18:58 UTC
Sabon Pira ministan kasar Tunisiya da ministocinsa sun saba layar kama aiki a fadar shugaban kasa.
Kamfanin Dillancin Labarun Faransa ya nakalto cewa; sabon pira ministan kasar Tunisiya, "Yusuf Shahid' da ministocinsa 26 da kuma mashawarta 14 sun saba layar kama aiki a gaban shugaban kasar Bajy Qa'ed al-Sibsy.
Ofishin shugaban kasar ta Tunisiya ya ce; A ranar litinin mai zuwa ce sabuwar gwamantin za ta fara aiki, bayan karbar madafun iko daga tsohuwar gwamnatin Habib al-Said da ministocinsa.
A ranar juma'ar da ta gabata ne dai mafi rinjayen 'yan majalisar kasar ta Tunisiya su ka kada kuri'ar amincewa da sabuwar gwamnati.
Tags