Jikkata Sojojin Faransa A Kasar Mali
Oct 14, 2016 05:37 UTC
Jikkata Sojojin Faransa A Kasar Mali
Sojojin Faransa shida sun jikkata sanadiyyar fashewar wata nakiya a arewacin kasar Mali.
Kakakin sojan Faransa a kasar Mali, Patric Stinger ya fada a jiya alhamis cewa; Nakiyar ta tarwatse ne a yankin Abibara da ke arewacin kasar wanda ya yi sanadin jikkatar sojoji shida.
A gefe daya, majiyar sojan Mali ta ce; sojojinta biyu sun mutu, a lokacin da motar da ta ke dauke da su ta ci karo da nakiya.
A makon da ya shude ma, an sanar da mutuwar tsohon shugaban kungiyar 'yan tawayen buzaye na kasar Mali, sanadiyyar tashin wani bom.
A shekarar 2015 ne aka yi sulhu a tsakanin gwamnatin kasar mali da 'yan tawayen buzaye, bisa shiga tsakanin majalisar dinkin duniya.
Tags