An kashe wani dalibin Jami'a a kasar Afirka ta kudu.
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i12748-an_kashe_wani_dalibin_jami'a_a_kasar_afirka_ta_kudu.
Bayan kwashe makuni na zanga-zangar Daliban jami'a a kasar Afirka ta kudu, fadar shugaban kasar ta sanar da kashe daya daga cikin daliban a kasar
(last modified 2018-08-22T11:29:07+00:00 )
Oct 21, 2016 17:53 UTC
  • An kashe wani dalibin Jami'a a kasar Afirka ta kudu.

Bayan kwashe makuni na zanga-zangar Daliban jami'a a kasar Afirka ta kudu, fadar shugaban kasar ta sanar da kashe daya daga cikin daliban a kasar

Kamfanin dillancin labaran Reuters daga Johannesburg ya nakalto fadar Shugaban kasar Afirka ta kudu a wannan juma'a na cewa Dalibin Jami'an ya rasa ransa ne sanadiyar hadarin Mota a jiya Alkhamis a  Pretoria birnin Siyasar kasar.

Rahotanni sun ce Jami'an 'yan sanda sun yi amfani da hayaki masu sanya hawaye wajen tarwatsa dariruwan daliban jami'a da suka tsuntsurundu a gaban Ofishin Shugaban Kasar Jacob Zuma  a birnin Pretoria domin  nuna adawarsu kan karin gudin karatu da magabatan jami'ar suke yi a ko wata shekara , tare da neman Gwamnati ta mayar da karatun kyauta a jami'o'in kasar gaba daya.

Bayan mutuwar Dalibin, labari ya watsu a cikin kasar kan cewa Jami'an 'yan sanda sun hallaka daya daga cikin shugabanin daliban Jami'a, lamarin da ya sanya fadar Shugaban kasar ta fito ta kara wata jita-jita tare da bayyana sanadiyar mutuwar ta sa.