Jami'an Tsaron Aljeriya Sun Tsaurara Matakan Tsaro A Yankin Gabashin Kasar
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i13183-jami'an_tsaron_aljeriya_sun_tsaurara_matakan_tsaro_a_yankin_gabashin_kasar
Majiyar tsaron Aljeriya ta sanar da cewa: Jami'an tsaron kasar sun yi dirar mikiya a yankin gabashin kasar ta Aljeriya da nufin zakulo wasu gungun 'yan ta'adda da suka kashe jami'in tsaron kasar.
(last modified 2018-08-22T06:59:10+00:00 )
Oct 31, 2016 07:37 UTC
  • Jami'an Tsaron Aljeriya Sun Tsaurara Matakan Tsaro A Yankin Gabashin Kasar

Majiyar tsaron Aljeriya ta sanar da cewa: Jami'an tsaron kasar sun yi dirar mikiya a yankin gabashin kasar ta Aljeriya da nufin zakulo wasu gungun 'yan ta'adda da suka kashe jami'in tsaron kasar.

Majiyar tsaron Aljeriya a yau Litinin ta sanar da cewa: Jami'an tsaron kasar sun yi dirar mikiya a garin Qasnadinah a yankin gabashin kasar da nufin zakulo wasu gungun 'yan ta'addan kungiyar Da'ish da ake kyautata zaton suna da maboya a yankin.

A ranar Juma'a da dare ne wasu gungun 'yan ta'addan kungiyar Da'ish su uku suka harbe wani jami'in dan sandan Aljeriya har lahira a wani gidan abinci a yankin na Qasnadinah tare da yin awungaba da bindigarsa.