Jami'an Sojin Kasar Ethiopia 3 Sun Rasa Rayukansu A Somalia
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i14140-jami'an_sojin_kasar_ethiopia_3_sun_rasa_rayukansu_a_somalia
Sojojin kasar Ethiopia 3 ne suka rasa rayukansu sakamakon wani bam da aka kai a yammacin jiya a kusa da birnin Kismayo da ke kudancin kasar Somalia.
(last modified 2019-08-10T14:54:46+00:00 )
Nov 20, 2016 05:47 UTC
  • Jami'an Sojin Kasar Ethiopia 3 Sun Rasa Rayukansu A Somalia

Sojojin kasar Ethiopia 3 ne suka rasa rayukansu sakamakon wani bam da aka kai a yammacin jiya a kusa da birnin Kismayo da ke kudancin kasar Somalia.

Shafin labarai na Misri Alyaum ya bayar da rahoton cewa, an kai harin bam din ne a lokacin da sojojin na Habsha da ke cikin rundunar kiyayaye sulhu ta kungiyar tarayyar Afirka suke sintiri a yankin, inda aka halak 3 daga cikin sojojin na Ethiopia.

Har yanzu dai babu wata kungiya da ta dauki alhakin kaddamar da wannan hari, amma tuni gwamnatin kasar ta Somalia ta dora alhakin hakan a kan kungiyar alshabab, wadda ta saba kai hare-hare makamantan hakan.