Najeriya: An Kashe 'Yan ta'addar Boko Haram 15 A Jahar Yobe
Wasu 'yan kungiyar Boko Haram 15 Sun halaka bayan da sojoji su ka kashe su a wani yunkurin kai hari a jahar Yobe.
Wasu 'yan kungiyar Boko Haram 15 Sun halaka bayan da sojoji su ka kashe su a wani yunkurin kai hari a jahar Yobe.
kamfanin dillancin labarun Reuters ya ambato cewa; An kashe 'yan ta'addar kungiyar ta Boko Haram ne a garin "Boni Yadi" da ke Jahar Yobe bayan da su ka yi kokarin kai hari akan wani sansanin soja a daren lahadi.
Bayan fada mai tsananin wanda ya ci rayukan sojoji biyar, yan kungiyar ta Boko Haram sun janye.
Sojojin Najeriya sun sanar da cewa; sun kori 'yan kungiyar ta Boko Haram daga cikin dajin Sambisa da ya zama tungarsu na tsawon shekaru.
Hare-haren da kungiyar ta ke kai wa a yankin arewa maso gabacin kasar ya yi sanadin kwararar yan gudun hijira a cikin gida da kuma waje, yayin da wasu da su ka kai 20,000 su ka kwanta dama.