An karya lagon boko haram a najeriya
Babban hafsan sojin Najeriya ya ce bayan kafa Rundunar hadin gwiwa na kasashen yankin tabkin Tchadi, an samu nasarar raunana mayakan boko haram
A yayin buda taron manyan hafsoshin soja na kasashen yankin tekun Tchadi (LCBC) da ya gudana jiya Talata a birnin Abuja na Najeriya, Babban hafsan sojin Najeriya Janar Abayomi Gabriel Olonisakin ya ce daga Lokacin da aka kafa Rundunar hadin gwiwa na kasashen yankin tabkin Tchadi (MNJTF),Shakka babu hare-haren da kungiyar boko haram ke kaiwa ya ragu sosai, sannan ya kara da cewa ya kamata a kara samun hadin kai a tsakanin Sojoji domin kawar da kungiyar boko haram gaba daya a yankin.
A nasa bangare babban komandan Rundunar hadin gwiwa na yankin Tabkin tchadi Manjo-janar Lamidi Adeosun ya ce duk da cewa an karya lagon mayakan kungiyar boko haram din a wasu yankuna to amma har yanzu akwai sauran rina a kafa don kuwa har yanzu suna ci gaba da kai hare-haren harin sari ka noke a wasu yankunan kasashen domin haka wajibi ne Sojojin su kara dagewa domin tabbatar da tsaro a yankin.
Rundunar hadin gwiwa na kasashen yankin tabkin Tchadi ta hada da Sojojin kasashen niger, nigeria, Kamaru da Tchadi.