Aljeriya Ta Kara Daukar Tsaurarar Matakai A Kan Iyakokinta
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i18292-aljeriya_ta_kara_daukar_tsaurarar_matakai_a_kan_iyakokinta
Babban hafsan hafsoshin sojin kasar Aljeriya Janar Ahmad Kai'd Saleh ya sanar da cewa, kasarsa ta fara daukar tsauraran matakai a kan iyakokinta, domin fuskantar barazanar da 'yan ta'adda ke yi wa kasar daga kasashen da ke makwaftaka da ita.
(last modified 2018-08-22T06:59:46+00:00 )
Mar 07, 2017 04:30 UTC
  • Aljeriya Ta Kara Daukar Tsaurarar Matakai A Kan Iyakokinta

Babban hafsan hafsoshin sojin kasar Aljeriya Janar Ahmad Kai'd Saleh ya sanar da cewa, kasarsa ta fara daukar tsauraran matakai a kan iyakokinta, domin fuskantar barazanar da 'yan ta'adda ke yi wa kasar daga kasashen da ke makwaftaka da ita.

Tashar talabijin ta Russia Today ta bayar da rahoton cewa, a zaman da babban kafsan hafsoshin sojin kasar ta Aljeriya janar Ahmad Kaid Saleh ya gudanar a jiya tare da sauran hafsoshi da manyan jami'an tsaron kasar, ya tabbatar musu da cewa, sabon shirin tsaron iyakokin kasar ya fara aiki, musamman a kan iyakokin kasar da kasashen Libya da Mali.

Daga farkon wannan shekara ta 2017, jami'an tsaron kasar Aljeriya sun kashe 'yan ta'adda fiye da 130 a kan iyakokin kasar da kasashen Mali da Libya, tare da kame wasu 225, tare da kame tarin makamai da suka hada da daruruwan bindigogi, da kuma makaman roka.