Kasashen Tunusiya Da Sudan Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Taimakekkeniya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i18778-kasashen_tunusiya_da_sudan_sun_rattaba_hannu_kan_yarjejeniyar_taimakekkeniya
Gwamnatocin kasashen Tunusiya da Sudan sun dauki matakin kara bunkasa alaka da taimakekkeniya a tsakaninsu ta hanyar rattaba hannu kan yarjeniyoyi har 22.
(last modified 2018-08-22T11:29:51+00:00 )
Mar 24, 2017 04:45 UTC
  • Kasashen Tunusiya Da Sudan Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Taimakekkeniya

Gwamnatocin kasashen Tunusiya da Sudan sun dauki matakin kara bunkasa alaka da taimakekkeniya a tsakaninsu ta hanyar rattaba hannu kan yarjeniyoyi har 22.

Kamfanin dillancin labaran China na Shin Huwa ya watsa rahoton cewa: A karshen zaman tattaunawa a tsakanin fira ministan Tunusiya Yusuf Shahid da takwararsa na Sudan Bakri Hassan Saleh jami'an kasashen biyu sun rattaba hannu kan tarin yarjeniyoyi har 22 da nufin bunkasa alaka da taimakekkeniya a tsakanin kasashensu musamman a bangarorin da suka shafi kiwon lafiya, yawon shakatawa, ilimi, musayar fasaha, gona da sauransu.

Har ila yau a bayan gudanar da zaman tattaunawan fira ministan kasar Tunusiya Yusuf Shahid ya bayyanawa manema labarai cewa: Daga nan zuwa watan Satumban wannan shekara ta 2017 za a fara samun safarar jirage kai tsaye a tsakanin kasashen Tunusiya da Sudan.

Tun a ranar Laraba da ta gabata ce fira ministan kasar Tunusiya Yusuf Shahid ya fara gudanar da ziyarar aiki na kwanaki biyu a kasar ta Sudan.