IS Ta Dauki Alhakin Kai Harinta Na Farko A Somaliya
May 24, 2017 06:39 UTC
Kungiyar ýan ta'adda ta IS ta dauki alhakin kai harin da ya yi sanadin mutuwar mutane biyar a yankin Bossasso dake arewacin kasar Somaliya
Wannan dai shi ne hari na farko da kungiyar ta dauki alhakin kaiwa a wannan kasa ta Somaliya.
A sanarwar data wallafa a shaffinta na Amaq kungiyar ta ce mutiminta ne ya kai harin da irin rigar boma-bomai.
A jiya Talata ne dan kunar bakin waken ya tarwatsa kansa a daidai lokacin da jamián tsaro suka tsare shi a daidai wajen wani shinggen bincike.
Tags