Damuwar MDD Kan Ci Gaba Da Rikicin Siyasa A Tsakiyar Afirka
Manzon Musaman Na MDD zuwa kasashen dake tsakiyar Afirka ya bayyana damuwar sa kan ci gaba da rikicin Siyasa a yankin.
Kamfanin dillancin labaran Xin Huwa na kasar China ya nakalto Francois Lounceny Fall manzon musaman na MDD zuwa kasashen yankin tsakiyar Afirka a wannan Laraba na cewa rikicin siyasa da wasu kasashen Afirka ke fuskanta so diyawa na samo asali ne kan yadda aka gudanar da zabe a kasashen ne wanda kuma hakan ke kawo cikas a zaman lafiyar kasar.
Mista Lounceny ya ce rikicin siyasa tsakanin Gwamnati da 'yan adawa a kasar D/Congo kan zaben Shugaban kasa, da kuma aiyukan ta'addanci na kungiyar Boko Haram a kasashen yankin tabkin Tchadi, abu ne da ya sanya MDD cikin damuwa.
Har ila Wakilin MDD ya ce halin da fararen hula ke ciki a wasu kasashen Afirka musaman ma wuraren da ake rikci abu ne mai tayar da hankali sosai.