An Bukaci Manyan Hafsoshin Sojin Najeriya Da Su Koma Maiduguri
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i22664-an_bukaci_manyan_hafsoshin_sojin_najeriya_da_su_koma_maiduguri
Mukaddashin Shugaban Najeriya Yemi Osibanjo ya umurci shugaban rundunar sojin kasa Janar Tukur Burutai da shugaban sojin sama Sadiq Abubakar da su koma Maiduguri domin magance matsalar tsaron da ake ci gaba da samu a yankin.
(last modified 2019-08-10T10:24:46+00:00 )
Jul 28, 2017 08:57 UTC
  • An Bukaci Manyan Hafsoshin Sojin Najeriya Da Su Koma Maiduguri

Mukaddashin Shugaban Najeriya Yemi Osibanjo ya umurci shugaban rundunar sojin kasa Janar Tukur Burutai da shugaban sojin sama Sadiq Abubakar da su koma Maiduguri domin magance matsalar tsaron da ake ci gaba da samu a yankin.

Wannan umarni na shugaban ya biyo bayan kisan soji 9 da wasu fararen hula da dama aka yi bayan wani kwanton bauna da 'yan Boko Haram din suka yi wa sojin kasar a kokarinsu na kwato masu binciken kasa na kamfanin mai na kasar da wasu malamai na jam'iar Maiduguri da Boko Haram din suka yi garkuwa da su a kwanakin da suka gabata. Tuni dai ma'aikatar tsaron kasar ta bakin ministanta Janar Mansur Dan Ali mai ritaya ta ce ta matsa kaimi a yaki da Boko Haram din musamman ma dai a wannan lokaci da suke zafafa kai hare-hare.

Jami’ar Maiduguri ta tabbatar da kashe wasu ma’aikatanta a harin da ‘yan kungiyar Boko Haram suka kai wa masu binciken man fetur a Magumari da ke cikin jihar Borno a Najeriya.