Kungiyar Boko Haram Ta Kai Harin Kunan Bakin Wake A Garin Dikwa
Mayakan kungiyar boko haram sun kai harin kunan bakin wake a garin Dikwa na jihar Borno dake arewa masu gabashin Najeriya.
Kamfanin dillancin labaran Reuteus ya nakalto kungiyar bada ajagin gaggauwa ta Najeriya na cewa a daren juma'ar da ta gabata, wani dan kungiyar boko haram ya kai harin kunar bakin wake a garin Dikwa na jihar Borno, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 14 tare da jikkata wasu 24 na daban.
Alkaluma na cewa daga farkon watan yuni zuwa yanzu, hare-haren ta'addancin kungiyar boko haram yayi sanadiyar mutuwar mutane akalla113.
Tun daga shekarar 2009 ne kungiyar boko haram ta fara kai hare-haren ta'addanci a Najeriya, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla dubu 20 tare da raba wasu sama da miliyan biyu da dubu 300 da mahalin su.