Sakatare Janar na MDD Na Ziyara A Afirka Ta Tsakiya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i25150-sakatare_janar_na_mdd_na_ziyara_a_afirka_ta_tsakiya
Yau Talata, babban sakatare MDD, Antonio Guterres ke fara wata ziyara ta kwanaki hudu a Afrika ta Tsakiya.
(last modified 2018-08-22T07:00:53+00:00 )
Oct 24, 2017 07:36 UTC
  •  Sakatare Janar na MDD Na Ziyara A Afirka Ta Tsakiya

Yau Talata, babban sakatare MDD, Antonio Guterres ke fara wata ziyara ta kwanaki hudu a Afrika ta Tsakiya.

Wannan ziyara dai na zuwa ne a yayin da kasar ta Afrika ta tsakiya ke kara tsunduma a cikin rikicin kusan shekara guda da ya yi sanadin mutuwar daririwan mutane.

Mista Guteres zai fara ziyara ne daga yankin Bangansu inda rikici ya fi kamari a 'yan watannin baya bayan nan.

A watan Nowamba mai zuwa ne ake sa ran kwamitin tsaro na MDD zai sabunta aiki da yawan tawagarsa ta wanzar da zaman lafiya a wannan kasa ta jamhuriya Afrika ta tsakiya.