Libya: An Yi Zanga-zangar Nuna Kin Amincewa Da Harin Garin Darnah
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i25312-libya_an_yi_zanga_zangar_nuna_kin_amincewa_da_harin_garin_darnah
Mazauna garin Darnah a arewa maso gabacin kasar ta Libya sun yi Zanga-zangar ne ta yin Allah wadai da harin da aka kai wa garinsu tare da kashe fararen hula.
(last modified 2018-08-22T11:30:56+00:00 )
Nov 04, 2017 12:06 UTC
  • Libya: An Yi Zanga-zangar Nuna Kin Amincewa Da Harin Garin Darnah

Mazauna garin Darnah a arewa maso gabacin kasar ta Libya sun yi Zanga-zangar ne ta yin Allah wadai da harin da aka kai wa garinsu tare da kashe fararen hula.

Bugu da kari masu Zanga-zangar sun yi tir da killace garin nasu da sojojin janar Halifa Haftar suka yi.

A daya gefen ma'aikatar harkokin wajen kasar Italiya ta bukaci da a gudanar da bincike akan laifukan yakin da aka tafka a cikin gari bayan gano gawawwakin mutane 36.

Tun bayan da kungiyar yarjejeniyar tsaro ta "Nato" ta kifar da gwamnatin Kaddafi a 2011, kasar Libya ta fada cikin rashin tsaro.

Kungiyoyin 'yan ta'adda  da suka hada da Dae'sh sun kafa iko da wasu garuruwa na kasar ta Libya da suka hada da Darnah.