An Zabi Sabon Shugaban Hukumar Zabe Na Kasar Tunisia
Nov 15, 2017 12:19 UTC
Majalisar dokokin kasar Tunisia ta zabi dan takatar neman shugabancin hukumar zaben mai zaman kanta na kasar, kuma dan jam'iyyar mai mulki ta Nida a matsayin sabon shugaban hukumar zaben.
Kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa ya bayyana cewa majalisar ta zabi mohammad Altalili Al-munsuri dan jam'iyyar Nida mai mulki a matsayin sabon shugaban hukumar zaben kasar. A shekara mai zuwa ce ake saran za'a gudanar da zaben lardunan kasar.
Kafin haka dai an shirya gudanar da zaben ne a ranar 17 ga watan satumba shekara 2017 da muke ciki, amma jam'iyyun adawa kasar sun bukaci a dage zaben zuwa ranar 25 ga watan Maris na shekara ta 2018 mai kamawa..
Tags