Afirka: "Yan Gudun Hijira 28 Sun Bace A Gabar Ruwan Moroko
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i25943-afirka_yan_gudun_hijira_28_sun_bace_a_gabar_ruwan_moroko
Kungiyar 'yan gudun hijira ta duniya ce ta sanar da bacewar 'yan gudun hijirar ta bakin kakakinta Joel Millman.
(last modified 2018-08-22T07:01:05+00:00 )
Dec 02, 2017 03:53 UTC
  • Afirka:

Kungiyar 'yan gudun hijira ta duniya ce ta sanar da bacewar 'yan gudun hijirar ta bakin kakakinta Joel Millman.

Joel Millman ta kara da cewa;  Wadanda suka bace din wani sashe ne na mutane 34 da kwale-kwalen da ke dauke da su ya tintsire. Tuni dai masu aikin ceto suka cetar da mutane 6 daga cikinsu.

Hukumar ta 'yan  gudun hijira ta sanar da cewa a cikin shekarar bana kadai mutane 174 ne suka halaka a cikin ruwan da ke tsakanin kasashen arewacin Afirka da Spain.

An sami karuwar masu mutuwa akan ruwan idan aka kwatanta shi da shekarar da ta gabata da bai wuce 121 ba.

Bugu da kari, rahoton na  hukumar da take kula da 'yan gudun hijirar ya ce;  Zuwa 29 fa watan Nuwamba adadin 'yan gudun hijirar da suka shiga cikin kasar Spain sun kai 19,000 da 688.